Mark 16

1Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana’iza. 2Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.

3Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?” 4Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.

5Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki. 6Sai ya ce masu, “Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi. 7Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku.”

8Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.

9Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta. 10Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka. 11Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.

12Bayan wadannan al’amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa’ilin da suke tafiya akan hanya. 13Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.

14Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu. 15Sai ya umarcesu cewa “Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta. 16Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.

17Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna. 18Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa.”

19Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah. 20Almajiransa kuma suka tafi ko’ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al’ajiba tare da su.

Copyright information for HauULB